Dakarun Najeriya da suke fafatawa a yankin Arewa Maso Gabas sun dakile wani hari da ‘yan kungiyar Boko Haram suka kai kauyen Goniri dake jihar Barno.
Wannan karon dai basu sha da dadi ba domin kafin ka ce tak Sojojin Najeriya sun fatattake su.
A dan kwanakinnan dai sojojin Najeriya sun yoi fama da hare-haren Boko Haram in da mafi muni da ga ciki shine wanda a kai bariki a sasawa kuma yayi sanadiyyar mutuwar wasu sojoji 11.
Discussion about this post