Hukumar Alhazai ta Kasa ta sanar da Kammala jigilar mahajjatan Najeriya kaf da suka yi aikin Hajji bana.
A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce jirgin karshe Max NGL 2110 ya baro filin jirgin sarki Abdulaziz da misalin Karfe 6:55 na safiyar litinin din nan da mutane mahajjata 172 daga jihar Kano, 76 daga jihar Ribas da ma’aikatan hukumar 30.
Jiragen Max Air, Medview da Nas Air ne suka yi jigilan yan Najeriya