• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

A BAJE A FAIFAI: Nazarin Ikirari 10 Da Buhari Ya Yi a Jawabin Ranar Tunawa da Samun ’Yanci

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
October 9, 2017
in Rahotanni
0
NAZARI NA MUSAMMAN:  BUHARI,  Mai Rabon Ganin Badi

Buhari in Office

Ranar Tunawa da samun ’yancin kasa, wacce aka shafe shekaru 57 ana bikin murnar zagayowar ranar, ta kasance wani dandali da gwamnati kan yi jawabai na hadin kan kasa, su bayyana ci gaban da su ka samar da kuma yin jawaban abin da za su samar wa al’umma a shekaru masu zuwa.

Sau da yawa wadannan jawabai kan fuskanci kalubale, musamman inda aka fahimci akwai dungu ko karkataccen zance, ko kuma inda masu nazari ke ganin kamar an nemi a yi wa ’yan kasa ‘yar-burum-burum.

Irin haka ta faru ga jawabin da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo yayin jawabin sa cikin 2005 da kuma Goodluck Jonathan a cikin 2012, inda ya ce nasarar yaki da cin hanci ta gwamnatin sa ce.

A jawabin da Shugaba Muhammadu Buhari ranar 1 Ga Oktoba, 2017, ya nemi ya yi gurmaden ikirarin aiwatar da wasu ayyuka ko tsare-tsaren da wasu ke ganin kamar akwai bukatar a tantace barcin makaho.

Kan haka ne PREMIUM TIMES HAUSA ta lalubo jawabin, inda ta fede shi dalla-dalla.

A jawabin Buhari, ya ce jam’iyyu ba su fara fara samun nasarar zabe a kananan hukumomi, jiha da tarayya ba, har sai lokacin mulkin sa. Wannan kuwa magana ba haka ta ke ba.

Ya kuma ce a lokacin sa hasken lartarki ya karu a cikin watan Satumba, fiye da zamanin kowane shugaba.

TSINKAYE NA 1:

Shugaban Kasa ya ce: Duk da an rika saida gangar danyen man fetur har dala 100, ana kuma hako har ganga milyan 2.1 a kowane rana kafin hawan sa mulki, an wayi an wawure kudaden, kuma babu kayan more rayuwar al’umma a cikin kasar nan.

“Sannan kuma aka bar mu babu ko taro a asusun gwamnati ba.’’

Binciken PREMIUM TIMES ya tabbatar da cewa a daidai lokacin da Buhari ya hau mulki cikin 2015, akwi har sama da naira bilyan 200 a cikin Asusun Jarin Nijeriya wanda aka kafa cikin 2011. Sannan akwai kuma wasu kudi har dala 2.1 da gwamnatin Buhari ta gada daga ribar gas da ake tattara wa jihohi.

Sannan kuma a lokacin da Buhari ya hau, akwai wata dala bilyan 2. 7 ta rarar cinikin danyen man fetur.

Yanzu kuma sai a sake bincike, shin da gaske ne akwai lokacin da aka rika sayar da gangar danyen man fetur har dala 100 kuma ana hako ganga milyan 2.1 a kowace rana tsakanin 1999 zuwa 2015?

Yayin da bincike da bayanan da PREMIUM TIMES ta samu daga hannun gwamnatin tarayya su ka nuna an dai saida gangar mai dala 61.o7, binciken ya kuma nuna cewa an rika hako har ganga milyan 2.3 a cikin wadancan shekaru.

TSINKAYE NA 2:

Buhari ya ce: “Kafin gwamnatin mu, bakon abu ne jam’iyya mai mulki ta fadi zaben gwamna, zaben Majalisar Tarayya ko na Majalisar Jihohi.’’

Wannan ikirari ba gaskiya ba ne. A zaben 2003 PDP ce rike da gwamnatin tarayya da kuma yawancin jihohi, saboda ita ce ta lashe zaben 1999.

A zaben 2007, jihohi 12 sun fada hannun jam’iyyun adawa, ciki kuwa har da ANPP, jam’iyyar Buhari a lokacin.

A zaben 2011 kuma jam’iyyun adawa sun kara cin jihohi, daga 12 a zaben 2007 zuwa 13 a 2011.

Adams Oshiomhole ya lashe zaben gwamnan Edo ranar 14 Ga Yuli, 2012, har ma ya fito ya gode wa Jonathan saboda abin da ya kira tsame hannun sa daga shiga cikin ruguguwar zabe.

Sai dai kuma a karkashin gwamnatin Buhari, gwamnan adawa daya ne ma ya taba yin nasara. An yi zabukan gwamnonin Bayelsa, Edo da Ondo, inda Edo da Ondo duk APC ce ta yi nasara, yayin da Bayelsa ce kadai jam’iyyar adawa, PDP ta lashe.

TSINKAYE NA 3:

Buhari ya ce sai a yi godiya ga sojjin kasar nan, saboda kakkabe Boko Haram da su ka yi, kuma su ka murkushe su, tare da yin galaba a kan su.

Ko a jabwabin san a 2016 ya bayyana haka. Amma a yanayin yadda ake gani, bai yiwuwa a ce an an gama da Boko Haram, domin har yau sun a kai hare-hare, kuma sojoji na ci gaba da yaki da su.

Ko kungiyar Afuwa ta Duniya ta ce daga watan Afrilu zuwa Satumba, Boko Haram sun kashe mutane 231 a Nijeriya.

TSINKAYE NA 4:

Buhari ya ce cikin Satumba 2017 karfin hasken lantarki ya karu zuwa migawat 7,001

To wannan ba haka abin ya ke ba, domin tun a cikin Janairu zuwa Agusta, 2015 ne hasken lantarki ya kai migawat 7,141.

TSINKAYE NA 5:

Buhari ya ce ya na murnar shaida wa ‘yan Nijeriya cewa yanzu an fara aikin hasken lantarki na Mambila, wanda shekara-da-sheakaru aka gagara a ciki gaba da
Wannan magana akwai gyara. Shi dai wannan aiki tun 1982 ne aka nemi fara shi, amma abin ya kakare. Lokacin gwamnatin Jonathan an nemi a fara, bayan an sabunta yarjejeniya, amma anin ya sake kakarewa.

A wannan lokaci na Buhari kuma, batun ya tsaya cak, har sai wata daya kafin jawabin sa, aka sanya hannu a yarjejeniya da wani kafanin kasar Chana, wanda shi ne zai kashe kudin sa har kashi 85 bisa 100, yayin da gwamnatin tarayya za ta bada kashi 15 kacal.

Kwangilar dai a kan dala bilyan 5.7 za a yi ta domin samar da lantarki migawat 30,000.

TSINKAYE NA 6:

Ikirarin Buhari cewa harkar takin zamani ta inganta a lokacin sa, sabanin shekarun gwamnatin da ta shude.

Buhari ya ce an farfado da masana’antun takin zamani 11, ana samun buhunan taki har milyan 7, kuma an killace dala milyan 150 na kudin da akan sayi taki a waje da kuma kebe wasu dala milyan 60 na tallafi shigo da taki.

Ya kuma bayyana cewa farashin takin zamani ya fadi daga naira 13,000 zuwa naira 5,500 kowane buhu mai nauyin kilogiram 50.

Tabbas za a iya cewa wannan jawabi na Shugaba Buhari gaskiya ne, domin jarjejeniyar takin zamani da ya kulla da kasar Morocco ta haifi da mai ido.

Sai dai kawai har yanzu wasu manoman sun kasa yarda cewa farashin taki ya sauka daga naira 13,000 zuwa 5,500 cif-da-cif.

TSINKAYE NA 7

Ikirarin Buhari cewa darajar naira ta tsaya kyam da kafafun ta, inda ya ce tun daga Fabrairu, 2017 da ta tsaya a 360 ko 365 a kowace dala daya, naira ba ta sake yin tashin gwauro zabo kamar da da ta kan kai har naira 525 ba.

Wannan ikirari na Buhari gaskiya ne. Domin hukumar kididdiga ta kasa ta tabbatar da cewa tsadar rayuwa ta ragu da kashi 9 bisa 100, idan aka kwatanta da 2015.

Sai dai kuma wani abin dubawa shi ne, a loakcin da Buhari ya hau mulki, ana saida dalar Amurka a kan naira 199.5 ne.

TSINKAYE NA 8:

Buhari ya ce ya bai wa jihoji har naira tiriliyan 1.642 tsakanin 2015 zuwa yau, domin su biya basussukan albashi, kudaden fansho da kuma tallafawa wajen kafa kananan masana’antu, wadanda aka yi watsi da su shekara da shekaru.

Wannan ikirari na sa gaskiya ne kwarai kuwa: 2015 ya ba jihohi naira bilyan 200, sai naira bilyan 441 cikin 2016, da kuma naira tiriliyan 1 cikin 2017.

TSINKAYE NA 9:

Buhari ya ce Gwamnatin sa kashe naira bilyan 500 wajen shirin ciyar da dalibai, samar da aikin yin a N-Power, tallafin Iyali na FHF, shirin samar da gidaje masu saukin kudi, da sauran su.
Wannan ikirari shi ma gaskiya ne matuka.

TSINKAYE NA 10:

Buhari ya ce su na aiki tukuru wajen kakkabe illar cin hanci da rashawa a kasar nan. Ya ce sun takaita satar kudi ta tsarin shigo da asusun bai daya, TSA, tsarin fallasa wadanda su ka wawuri kudi, wato hura usur, killace bayanan biyan albashin ma’aikata da sauran su.

Wannan batu na tsarin TSA a gaskiya ba shi ne ya kirkiro shi ba. An kirkiro shi ne lokacin gwamnatin Jonathan. Don haka ba za a iya cewa wani sabon abu ne gwamnatin Buhari ta kirkiro.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ya zuwa Janairu 2015, sama da hukumomin gwamnati 500 su ka fara amfani da tsarin TSA, wanda aka shigo da shi tun cikin 2012.

Amma tsarin hura wa wadanda su ka wawuri kudin gwamnati usur, ana fallasa su, Shugaba Buhari ne ya kirkiro shi.

Tags: AbujaBuhariHausaHausa Premium TimesLabaraimulkiPREMIUM TIMES
Previous Post

‘Yan sandan sun yi zanga-zangar rashin biyan su albashi

Next Post

Mutane 7 sun rasu sanadiyyar kifewan jirgin ruwa a jihar Kebbi

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Mutane 7 sun rasu sanadiyyar kifewan jirgin ruwa a jihar Kebbi

Mutane 7 sun rasu sanadiyyar kifewan jirgin ruwa a jihar Kebbi

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin jari mai kauri ya sa noma na ya ƙi gaba, ya ƙi baya – Wata mace mai himma
  • CIRE TALLAFIN MAI: Kungiyoyin ma’aikatan lantarki, Ƴan jarida da na Kwadago za su tsunduma yajin aiki daga ranar Laraba
  • Yadda bashin Dala Miliyan 19.3 na Bankin Musulunci ya bunƙasa noma a ƙananan hukumomin Kano 44 – Hamisu, Kodinetan KSADP
  • Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati
  • Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.