Kotun karan dake Iyaganku jihar Oyo ta gurfanar da wani magidanci mai suna Samson Ayodele da ta kama da laifin aikata fiyade ga wata yarinya ‘yar shekara 12 a dakinsa.
Wanda ya shigar da karan Folake Ewe ya fada wa kotun cewa Samson ya aikata hakan ne ranar 18 ga watan Satumba da misalin karfe 2 na rana.
Ya ce Samson ya zolayi yarinyar ne har ya kai ta dakinsa dake Adeyi Avenue Bodija Ibadan sannan ya danne ta da karfin tsiya.
Alkalin kotun I.O.Olanipekun ya yanke hukuncin daure Samson a kurkuku har sai bayan ya saurari shawarwari daga bangaren da ake gurfanar da mutane masu aikata irin hakan.
Alkalin ya kuma daga sauraron karan zuwa 19 ga watan Oktoba.
Discussion about this post