Ali Ahmadu dai wani yaro ne dan shekara 6 da haihuwa mazaunin garin Chibok da Allah yasa zai ci gaba da tafiya a rayuwarsa.
Ali ya fada hannu ‘Yan Boko Haram ne a garin Chibok, inda suka taka shi da Baburansu har ya karya kashin bayan sa.
Wata kungiya mai zaman kanta ne ta dauki nauyin kai Ali wata Asibiti dake kasar Dubai domin yi masa aiki ko zai iya sake tafiya.
Cikin Ikon Allah Kuwa aiki yayi kyau domin ga Ali nan har ya fara takawa.