Jami’ar Bayero dake Kano ta gano cogen takardun shiga jami’ar da wasu daliban jami’ar su kayi wanda hakan ya sa aka sallamar su.
Hukumar jami’ar ta yi hakan ne bayan ta gudanar da bincike akan takardun daliban sannan ta yanke shawaran daukan wannan matakin.
Ga sunayen daliban.
1. Yahaya Shuaibu Muhammad
2. Khadija Ibrahim
3. Yusuf Usman Abdullahi
4. Mansura Muhammad Danjuma
5. Sumayya Said Ismail
6. Ado Auwalu Malam
7. Aliyu Musa
8. Aminu Muhammad Usman
9. Ibrahim Aminu Dahiru
10. Surajo Ahmad Adamu
11. Aliyu Haruna
12. Nuruddeen Yunusa Kuta
13. Anas Abdullahi Muhammad
14. Nusaiba Ado Gwarjo
15. Idris Kawuwa
16. Saidu Araga Ahmed
17. Rafatu Abdulkareem
Bayan hakan hukumar jami’ar ta yi wa wasu dalibai uku afuwa wanda ya hada da Abdulmajid Sale, Mahmud Danladi da Yusuf Abdulmateen bayan ta warware matsalolin dake tattare da takardun shigan su jami’ar.
Ibrahim Idris Yakasai ya sami takardar sallama bayan an gano cewa bai ciki sharudan shiga jami’ar ba sannan ta dakatar da gudanar da bincike akan wani Abubakar Sarkin Saidu.