Yau aka fara taron hadin gwuiwa kannkiwonn lafiya, wanda Cibiyar Gudanar da Binciken Kwakwaf A Aikin Jarida, Cibiyar Wayar da kula da lafiyar yara da iyali da kuma Project Pink Blue su ka shirya a Abuja.
Wannan taro da ake gudanarwa kan kiwon lafiya, zai kasance Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo ne shugaban taron, yayin da Ministan Lafiya, Isaac Adewole ne mai masaukin baki.
Za a gudanar da taron a Cibiyar Taro ta Shehu Yar’Adua da ke Abuaja, wanda tuni kuma an fara gudanar da shi.
Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ne zai gabatar da jawabin bude taro.
PREMIUM TIMES HAUSA za ta rika kawo muku bayanan yadda taron ke gudana daki-daki.
Discussion about this post