Gwamnatin Jihar Kaduna ta sanar da cewa zata raba na’urorin komfuta da Tablet dake kunshe da litattafai 300 ga makarantun jihar.
Kwamishinan Ilimi na jihar Andrew Nok ne ya sanar da haka da yake kaddamar da shirin a Zariya.
Nok Yace gwamnati za ta fara da samarwa makarantun kwana da ke jihar ne inda bisa ni kuma za ta raba ma sauran makarantu.
Kwamishinan y ace gwamnati za ta karo wadannan na’urori domin rabawa sauran makarantun jihar.
Discussion about this post