Ministan kiwon lafiya Isaac Adewole ya bayyana wasu daga cikin dalilan da ya sa ya dakatar da shugaban hukumar inshorar lafiya lafiya ta kasa NHIS Usman Yusuf shine don korafe-korafen da ake tayi a kan sa na yin sama da fadi da kudaden ma’aikatar da kuma zargi da akeyi masa na aikata wasu laifuka da ya saba dokar hukumar.
Minista Isaac Adewole ya ce ya dakatar da Usman Yusuf na tsawon watanni uku ne saboda a sami damar gudanar da bincike kan zargin da ake yi a masa.
Ya yi kira ga ma’aikatan hukumar da su tabbata sun saka ido akan takardun ma’aikata har zuwa a kammala bincike.
Ministan kiwon lafiya Isaac Adewole ya ce wasu daga cikin dalilan da ya sa ya dakatar da shugaban hukumar inshorar lafiya lafiya ta kasa NHIS Usman Yusuf shine don korafe korafen da ake tayi akansa na sama da fadi da yayi da wasu kudaden ma’aikatan da kuma zargi da akeyi masa na aikata wasu laifuka da ya saba dokar ma’aikatar.
Minista Isaac Adewole ya ce ya dakatar da Usman Yusuf na tsawon watanni uku ne saboda a sami damar gudanar da bincike akan zargin da akeyi a kansa.
Ya yi kira ga ma’aikatan hukumar da su tabbata sun saka ido akan takardun ma’aikatan har zuwa a kammala bincike.
Discussion about this post