Wani Basarake a jihar Zamfara mai suna Usman Kabir Danbaba ya zai yi zaman gidan yari bayan kama shi da kotu tayi da damfarar wasu da yayi na kudi sama da naira Miliyan 1 cewar zai sama musu lasisin iya hakar ma’adinai a jihar Zamfara.
Hukumar EFCC ce ta maka shi a wata Kotu dake zama a jihar Kano.
Danbaba ya amsa laifinsa daga baya bayan ya musanta haka a farkon zama kotu.