Hukumar shirya jarabawar kammala makarantar sakandare WAEC ta sanar da cewa duk wanda bai karbi sakamakon jarabawarsu na WAEC ko GCE bayan shekaru hudu da rubuta jarabawar ba zai biya kudi kafin ya karbi sakamakon.
Wani Jami’I a hukumar, Demianus Ojijeogu ne ya sanar da haka da ya ke zantawa da kamfanin dillancin labarai a wata hira ta wayan tarho a ranar Alhamis a Abuja.
Demianus Ojijeogu ya ce kudin da za a biya ba masu yawa kudine da muka masa lakabi da kudin ajiya.
‘’Menene dalilin rubuta jarabawar da ba za a karbi sakamakon ta ba’’.
Ga yadda kudin yake da abinda za aka biya duk bayan shekara.
1 – Shekara daya zuwa hudu – Naira 3,500.
2 – Shekaru biya zuwa tara – Naira 8,900.
3 – Shekaru 10 zuwa 14 – Naira 13,500.
4 – Shekaru 15 zuwa 19 – Naira 18,500.
5 – Shekaru 20 zuwa sama – Naira 23,500.
Demianus Ojijeogu ya ce cikin abubuwar da za a bukata kafin a karbi sakamakon jarabawar sun hada da hoton fasfo daya, takardar sakamakon jarabawar da aka samo daga yanar gizo da takardar shaidar ratsuwar daga kotu.
Discussion about this post