• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Zaben MOPPAN: Maikano ya doke Lere, Ciroma

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 11, 2017
in Nishadi
0
Zaben MOPPAN: Maikano ya doke Lere, Ciroma

A ranar Lahadi ne aka rantsar da sabon Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Masu Shirya Finafinai ta Kasa, MOPPAN, bayan an gudanar da zabe a Kano.

Sabon Shugaban, Abdullahi Maikano, ya kada abokan takarar sa biyu, Yakubu Lere da Al’amin Ciroma. Dukkan ‘yan takarar su uku daga Kaduna suke, kasancewa a wannan zaben an kayyade cewa daga bangaren Kaduna shugaban kungiyar zai fito.

Tashin farko dai takara ta yi zafi kusan fiye da sauran zabukan kungiyar da aka taba yi a baya, saboda wasu dalilai. Kowane dan takara ya tashin haikan ya na yakin neman zabe, a Kaduna, Kano da sauran jihohin Arewa.

Zaben da aka kada kuri’a da asubahi, bayan an kashe dare ana tantance ‘yan takara da masu zabe, ya zo da bazata, ganin yadda Maikano ya yi wa sauran ‘yan takara rata mai nisan gaske.

Yayin da ya zo na daya da kuri’a 57, Lere ne ya zo na biyu da kuri’u 54, shi kuma na uku, wato Al-amin Ciroma ya samu kuri’u 13. Zaben dai wakilai 5 daga kowace na Arewacin kasar nan masu ruwa da tsaki a harkar fim suka jefar kuri’un, a zaben da aka gudanar cikin zauren taron Otal din Royal Tropicana, Kano.

MOPPAN, wacce a Turance ke nufin Motion Pictures Practitioners Association of Nigeria, kungiya ce mai kunshe da sauran kungiyoyin ‘yan fim tun daga na wasa, furodusoshi, editocin finafinai, daractoci da sauran su.

Alhaji Abdulkarim Mohammed, shugaban kamfanin shirya finafinai na Moving Image ne shugaban kungiyar na farko, daga shi sai Alhaji Sani Mu’azu sai kuma Dakta Umar Faruq Jibrin, mai kamfanin Kwality, malamin jam’a a BUK, kuma tsohon kwamishinan yada labarai na jihar Kano, wanda shi ya sauka, bayan an kafa kwamitin riko ne daga baya aka shirya zabe.

Wannan zabe na MOPPAN ya dau zafi ta hanyoyi da bangarori da dama. Na farko dai a tsakanin su kan su ‘yan takara, a baya an sha samun takun-saka da ‘yar tsama a tsakanin Lere da Maikano, dukkan su manyan furodusoshi a Kaduna. Dama kuma Maikano ya dade ya na harin shugabancin kungiyar, bai samu ba, sai a wannan karo.

Wata matsala wacce ita ce ake zargin alamomi ko dalilan zargin tsoma bakin gwamnatin Jihar Kaduna a cikin sha’anin zaben, ita ce batun Lere, wanda a zahiri ya yaki takarar Nasiru El-Rufai a 2015, bakin rai bakin fama, a matsayin sa na shugaban gidan radiyo mallakar gwamnatin jihar Kaduna, a zamanin mulkin Ramalan Yero.

Idan za a iya tunawa, Lere ne jami’in gwamnati na farko da aka fara sallama daga cikin gyauron gwamnatin Ramalan Yero, kasancewar sa dama nadi ne aka yi masa na siyasa, ba takamaimen ma’aikacin gwamnati ba ne.

PREMIUM TIMES HAUSA ta tabbatar da cewa mai ba Gwamnan Kaduna Shawara a fannin ingata harkokin matasa, ta gayyaci ‘yan takarar uku zuwa ofishin ta, inda bayan ta tabbatar musu cewa gwamnati ba ta goyon bayan kowa a cikin su, sai ta gabatar musu da wata takardar da ke dauke da sunayen su, kuma ta ce kowa ya sa hannu a kan takardar, cewa ya yi alkawarin ba zai haddasa tarzoma ko wani rikici, kafin da kuma bayan zabe ba.

Daya daga cikin ‘yan takarar ya tabbatar mana faruwar haka, inda kuma ya ce kafin su shiga ofishin sai da aka kwace wayoyin kowanen su bayan an caje su. Dama kuwa kowa ya je da wasu daga cikin na hannun damar sa a wajen kamfen.

Jami’ar ta bayyana musu cewa su na da rahoton jami’an tsaro da ke hasashen cewa wani ko wasu daga cikin ‘yan takarar zai yi amfani da matasa ‘yan baberiya domin a yamutsa harabar zaben, zargin da kowanen su ya musanta.

Yayin da ake kallon Lere a matsayin rikakken dan adawar gwamnatin jihar Kaduna, shi kuma Al-amin an yi masa kallon makiyin gwamnatin jihar Kano.

Ganin yadda Ciroma ke da goyon bayan wakilan zabe da dama, an yi mamakin yadda ya fadi zaben kuma aka yi masa mummunar rata. Sai dai kuma bayan kammala zaben wata kwakkwarar majiya a Kano, ta shaida Premium Times Hausa cewa ba abin mamaki ba ne ba shi idan Ciroma ya fadi zaben.

Majiyar ta ce akwai da yawan masu ruwa da tsakin harkar fim wadanda ba su ji dadin yadda ya rika yin rubuce rubuce ya na sukar MOPPAN ta jihar Kano, dangane da dakatar da Rahma Sadau daga harkar fim da aka yi ba.

Wasu sun yi zargin cewa su na gudu kada bayan zaben sa ya ce ya soke dakatarwar da aka yi wa Rahma.

Hausawa na cewa bayan tiya, akwai wata caca. Tun ranar Juma’a da rana sai labari ya rika yawo cewa an ga wasu jami’an gwamnatin jihar Kaduna su na gilmawa a cikin harabar Otel din Royal Tropicana, inda aka tsara cewa a nan za a yi taro. Wata majiya kuma ta ce a Otel din Ni’ima su ka sauka musammam. Sai dai kuma sun shaida wa ‘yan fim din da suka san su cewa ba zaben ya kai su Kano ba, sun he yin wani sha’ani ne na daban.

Akwai alamomin da suka rika nuna cewa wasu manyan harkokin finafinai sun fi karkata a kan Abdullahi Maikano.

Babbar matsalar kungiyar MOPPAN a yanzu dai biyu ce. Na farko dai wannan gidan jarida ta ji daga kwakkwarar majiya cewa ko naira dubu goma babu a asusun kungiya har zuwa ranar zabe. Sannan kuma akwai matsalar shawo kan magoya bayan ‘yan takara. A fili ta ke cewa makusantan Al-amin Ciroma sun fusata sosai, kuma wasun su sun yi zargin cewa a daren da za a fara jefa kuri’a an canja wa wasu ‘yan takara ra’ayin wanda za su zaba.

Jerin Sunayen Shugabannin MOPPAN Na Kasa

1. Shugaba:

Abdullahi Maikano

2. Mataimaki Na 1.

Salisu Mu’azu

3. Mataimaki Na 2.

Nasiru B. Muhammad

4.Mataimaki Na 3.

Adamu Jahun

5. Sakatare Na Kasa:

Ahmed Alkanawy

6. Mataimakin Sakatare:

Abdullahi Dan Asabe

7. Ma’aji:

Nura Hussaini

8. Jami’in Hulda Da Jama’a:

Maikudi Cashman

9. Sakataren Kudi:

Bello Achida

10. Sakataren Shirye-shirye:

Ahmed Hashim

11. Mai Binciken Kudi 1:

Haruna Goodwill

12. Mai Binciken Kudi 2:

Tijjani Faraga

Karanta labarin a shafinmu na Turanci a nan: KANNYWOOD SPECIAL: New MOPPAN leadership grapples with challenges after acrimonious elections

Tags: CiromaFaruq JibrinHausaLabariLereMaikanoMOPPANMotion Pictures Practitioners Association of NigeriaNajeriyazabe
Previous Post

Buhari ya tafi kasar Britaniya ganin likitoci

Next Post

Zaman lafiya ya dawo Kaduna

Next Post
Kaduna crisis

Zaman lafiya ya dawo Kaduna

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ‘Yan sanda sun ce gidan da mafusata su ka kai wa hari a Bauchi ba na Shugaban INEC ba ne
  • SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima
  • SABON RIKICIN PDP: ‘Ko dai ka janye dakatarwar da ka yi min, ko na fice na bar maka jam’iyyar’ -Gargaɗin Shema ga Ayu
  • TAYA MURNA: Manyan Malaman Kaduna sun yi buɗe baki da sabonn gwamnan Kaduna, Uba Sani
  • Kotun Ƙoli ta ƙaryata rahoton Cif Jojin Najeriya ya yi ganawar sirri da Tinubu a Landan

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.