• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RAHOTO NA MUSAMMAN: Harkallar Naira Biliyan 16: Yadda EFCC ta kwace asusun bankin Hukumar Tsaro ta NIA

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 15, 2017
in Babban Labari
0
RAHOTO NA MUSAMMAN: Harkallar Naira Biliyan 16: Yadda EFCC ta kwace asusun bankin Hukumar Tsaro ta NIA

Hukumar Hana Laifukan Harkalla Da Zambar Kudade, EFCC, ta kwace asusun ajiyar kudade na Hukumar Leken Asiri ta Kasa, NIA a ranar Juma’ar da ta gabata. Hakan ya biyo bayan wani gagarimin bincike ne da aka fara dangane da naira bilyan 13 da EFCC ta bankado a wani gida a Ikoyi, Lagos, kudin da aka hakkake mallakar hukumar NIA ne.

Wadannan makudan kudade da shugaban hukumar Ayodele Oke ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa mallakar hukumar sa ce, sun kai ga dakatar da shi daga aiki bayan an kafa kwamitin binciken yadda aka yi wadannan makudan kudade suka je cikin gidan da aka bankado su.

Ana wata kuma sai ga wata, wata majiya ta jami’an tsaro ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa, a ranar Juma’ar da ta gabata, jami’an EFCC sun tilasta wa daraktan kula da harkokin kudi da mulki na hukumar tsaro ta NIA, ya damka gaba dayan sirrin adadin kudade da bayanan da ke cikin asusun ajiyar hukumar ga wani jami’in soja da ke aiki a ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara a Fannin Tsaro.

EFCC dai ta ce wannan jami’in soja mai suna Burgediya Janar Ja’afaru Mohammed shi ne zai zama jami’i na riko da zai kula da harkar kula da asusun bankin da kuma harkokin kudi na hukumar tsaron ta NIA.

Wannan kwatagwangwama dai ta kai ta kawo ne har ta kai cikin satin da ya gabata, jami’an EFCC sun yi wa wasu jami’an tsaron NIA hudu tambayoyin kwakwaf.

PREMIUM TIMES ta boye sunayen wadannan jami’ai da aka yi wa tambayoyi dangane da harkallar kudade a hukumar ta NIA, saboda bayyana sunayen na su zai iya shafar binciken da ake gudanarwa.

Majiyoyi da dama sun bayyana wa wannan jarida cewa, sau biyu a cikin makon da ya gabata, hukumar EFCC na yin kokarin damka asusun ajiyar NIA a hannnun Burgediya Mohammed, amma sai jami’an NIA su ki ba shi hadin kai.

PREMIUM TIMES ta ji cewa ganin yadda NIA ta ki amincewa da damka ragamar harkokin kudaden hukumar ga Burgediya Mohammed ne ya sa ta gayyaci daraktan kula da harkokin kudade na hukumar, da shi da wasu mukarraban sa guda biyu zuwa ofishin ta. Bayan sun shafe awoyi masu yawan gaske ne su na amsa tambayoyin da aka rika sheka musu, ne aka sake su.

An kuma tabbatar da cewa a cikin makon da ya gabata din, sai da EFCC ta dira a hedikwatar NIA din ta yi wa wasu jami’ai tambayoyi masu zafin gaske.

A ranar Juma’ar da ta gabatan dai ne EFCC ta gayyato daraktan kula da harkokin kudin inda ta tsare shi, tsawon awoyi da dama, inda daga bisani jami’an na EFCC suka dauke shi zuwa hedikwatar NIA din kuma suka tilasta shi ya damka sirrin asusun ajiyar kudade na hukumar a hannun Burgediya Mohammed.

EFCC Ta Yi Katsalandan?

Duk da cewa wannan sabon mataki da ka dauka ya samo asali ne daga bankado zunzurutun kudade har naira bilyan 13 na NIA da aka karkatar aka kimshe a wani gida a Lagos, wasu jami’an tsaro da dama su na dora alamar tambaya a kan irin wannan bincike da su ke ganin kamar katsalandan ne EFCC ta yi a cikin sha’anin hukumar leken asiri ta kasa, NIA din. Su na masu kafa hujja da doka ta 2004 da ta kafa hukumar, wacce su ka ce ta yi nuni da cewa an haramta yi wa NIA katsalandan.

“Sashe na 12(1) na dokar NIA ta 1 da ke cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya ya nuna cewa babu zancen yin katsalandan a harkokin kudin hukumar NIA, haka ba a yarda wata hukuma daga waje ta shiga ta kididdige ko ta yi bincike a asusun ba……”

Wannan doka dai tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Abdulsalami Abubakar ne ya wanzar da ita a cikin 1999, kuma aka kakaba ta, ta zama doka a karkashin dokar Hukumar Tsaro ta NSA.

Gargadi:

Duk da wannan dokar da aka tanadar, ‘yan Nijeriya da dama sun rika tattauna abin da ka iya zuwa ya zo dangane da binciken asusun hukumar liken asiri ta NIA, wadda ake zargin daga asusun ta ne aka gabji makudan kudaden da aka kimshe a wani gida a Lagos, har naira bilyan 13, wadanda EFCC ta bankado.

Ko a cikin watan Afrilu da ya gabata, sai da tsohon ministan harkokin waje, Farfesa Bolaji Akinyemi ya shawarci shugaba Muhammadu Buhari da ya yi taka-tsantsan a kan fallasa hukumar leken asiri ta NIA.

Akinyemi dai ya taba kula da harkokin NIA kafin a dauke hukumar kacokan a maida ta a karkashin ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara a Fannin Tsaro, NSA.

Ba Akinyemi kadai ke da wannan ra’ayin ba, har da Cif Emeka Anyeaku, tsohon Shugaban Majalisar Kasashe Rainon Ingila, wato Commonwealth of Nations.

Sai dai kuma ‘yan Nijeriya da dama na masu ra’ayin cewa bai kamata a ce ba za a binciki ko ma wace hukuma ba ce da aka samu da harkallar makudan kudade har naira bilyan 13 ba.

Kwamitin da shugaban kasa ya kafa a karkashin mataimakinsa Yemi Osinbajo, ya tura jami’ai biyu daga ofishin Akanta Janar na Tarayya, domin su domin su yi filla-filla da asusun ajiyar Hukumar NIA.

Cikin makon da ya gabata dai, wasu jami’ai sun bayyana wa PREMIUM TIMES cewa sun damu kwarai dangane da yadda aka yi wa NIA katsalandan wajen afkawa cikin sanin sirrin harkokin kudaden su.

Wata majiyar jikin ofishin Shugaban Kasa ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa tsoffin shugabannin hukumar NIA su uku, sun hadu sun dunguma sun je wurin mataimakain shugaban kasa inda suka yi masa bayanin ra’ayin su.

PREMIUM TIMES ta nemi jin ta bakin EFCC, amma ba su ce komai ba, dangane da jawabin da aka nemi su yi a kan wannan kwatagwangwama. Kakakin yada labaran ta, Wilson Uwujaren bai dauki waya ba a lokacin da aka kira shi, haka kuma bai maido amsar sakon tes da aka yi masa ba, bayan da farko ya yi alkwarin zai maida amsa nan take.

Tags: EFCCHausaHausa LabaraiIbrahim MaguLabaraiMaguNIA
Previous Post

YUNWA: Gwamnatin Najeriya na Bukatar ta maida hankali sosai wajen wadata kasa da abinci

Next Post

Jamila Nagudu ta za ma Jakadiyar sanadarin abinci, Vedan

Next Post
Jamila Nagudu ta za ma Jakadiyar sanadarin abinci, Vedan

Jamila Nagudu ta za ma Jakadiyar sanadarin abinci, Vedan

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • A BARI YA HUCE KE KAWO RABON WANI: APC ta ɗage ranar tantance ‘yan takarar shugaban kasa
  • FIDDA-GWANIN SHUGABAN ƘASA 2023: Yadda gwamnoni ke baki-biyu tsakanin su ‘yan naci, ‘yan mai-rabo-ka-ɗauka da ‘yan idan-ta-yi-ruwa-rijiya
  • Ƴan sanda sun kashe masu garkuwa da mutane uku a Adamawa
  • Dalilin da ya sa za mu ƙirƙiro gundumomi 268 a jihar Filato – Lalong
  • TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.