• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

    ZAƁEN GWAMNA A KANO: Har ƙarfe 12 na ranar zaɓe ana ta raba wa talakawa taliya da atamfofi

    ZAƁEN GWAMNA A KANO: Har ƙarfe 12 na ranar zaɓe ana ta raba wa talakawa taliya da atamfofi

    Election Materials

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: Faɗa ya ɓarke lokacin da ‘yan-ta-kife su ka kutsa ofishin INEC, su ka ragargaza akwatin zaɓe

    WHO ta tallafa wa kananan hukumomin Kaduna da Babura

    Kotu ta bada belin barawon babura 100 kan naira miliyan 1

    Thugs-attack-collation

    KASHE-KASHEN JAJIBIRIN ZAƁEN GWAMNONI: An kashe mutum uku a harin da ‘yan daba su ka tarwatsa taron APC a Oyo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

    ZAƁEN GWAMNA A KANO: Har ƙarfe 12 na ranar zaɓe ana ta raba wa talakawa taliya da atamfofi

    ZAƁEN GWAMNA A KANO: Har ƙarfe 12 na ranar zaɓe ana ta raba wa talakawa taliya da atamfofi

    Election Materials

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: Faɗa ya ɓarke lokacin da ‘yan-ta-kife su ka kutsa ofishin INEC, su ka ragargaza akwatin zaɓe

    WHO ta tallafa wa kananan hukumomin Kaduna da Babura

    Kotu ta bada belin barawon babura 100 kan naira miliyan 1

    Thugs-attack-collation

    KASHE-KASHEN JAJIBIRIN ZAƁEN GWAMNONI: An kashe mutum uku a harin da ‘yan daba su ka tarwatsa taron APC a Oyo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yadda aka yi tirka-tirka da tuggun maye gurbin marigayi Abacha a fadar Aso Rock -Janar Bamaiyi

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 6, 2017
in Babban Labari
1
Yadda aka yi tirka-tirka da tuggun maye gurbin marigayi Abacha a fadar Aso Rock -Janar Bamaiyi

Tsohon Hafsan Hafsoshin sojojin Nijeriya, Janar Ishaya Bamaiyi, ya bayar da labari tiryan-tiryan na yadda manyan hafsoshin kasar nan suka rika tafka rikici, tuggu da tirka-tirkar wanda zai zama shugaban kasa bayan mutuwar tsohon shugaban kasa, Janar Sani Abacha, wanda ya mutu ranar 8 Ga Yuni, 1988.

Bamaiyi, wanda tsohon Laftanar Janar ne, ya bayyana wannan kwamacala ce a cikin wani littafi da ya rubuta da Turanci, mai suna “Vindication of a General” wanda aka kaddamar a ranar Alhamis da ta gabata, a Abuja.

Ya yi bayanin cewa, bayan rufe gawar Abacha a Kano, a wannan ranar sai manyan hafsoshin sojojin kasar nan suka koma Majalisar Koli a fadar Shugaban Kasa, inda suka yi taro domin a fito da wanda zai zama shugaba.

Ya ce duk da cewa shi ba shi da muradin son zama shugaban kasa, sai aka fi maida karfi wajen zaben Babban Hafsan Tsaron Kasa na lokacin, Abdulsalami Abubakar, Ministan Abuja a lokacin, Jeremiah Useni da kuma shi Bamaiyi din. Haka Bamaiyi ya bayyana a cikin shafi na 252.

“Ban taba sha’awar rike wani mukami na siyasa ba, domin na guji hakan tun tuni, kuma ba ni da niyyar zama shugaban kasa. Haka na bayyana wa manyan sojojin da ke wurin, wadanda su ka jajirce cewa ni ne zan zama shugaba a lokacin, cikin su kuwa har da Janar Victor Malu, Magashi da Patrick Aziza.”

“A lokacin ina sane da cewa wasu kananan hafsoshi wadanda ba su so na zama shugaban kasa, saboda sun san ba zan amince su ci gaba da kasancewa a cikin aikin soja ba.”

Ya kara da cewa duk da rashin sha’awar shugabanci da ya yi, matsalar da ya ke da ita dangane da Abdulsalami, ita ce an taba kama shi dumu-dumu da laifi bayan wata kotun soja da aka kafa ta binciki yadda ya yi harkallar kudaden albashin sojoji tsakanin 1970 zuwa 1972. Wannan dalilin ne ya ce ya yi tunanin da wuya idan ma ya ce a zabi Abdulsalami, wasu ba za su amince ba.

Bamaiyi ya ce “amma maimakon a daure Abdulsalami shekara biyu ko a kore shi, ko a rage masa mukami, sai ya hada kai da shugaban kwamitin binciken marigayi Kanar Nenger, wanda dama ajin su daya a Sakandaren Bida, aka sassauta masa hukunci zuwa jan-kunne.”

Bamaiyi ya kara da cewa, ana fara wancan taro a fadar Aso Rock, sai kawai Abdulsalami ya tashi ya fara raba wasu takardu, kamar ya na nufin zabe ne za mu yi kenan mu fitar da shugaban kasa.

Ya kuma ce mana, “Wani ba zai zabi duk wanda aka taba samu da aikata laifi ba a matsayin shugaban kasa. Don haka zabe za mu yi a nan mu fitar da shugaban kasa. Kenan batun wanda zai gaji Abacha ya fado kai na, kuma wasu manyan hafsoshi duk su ka ce min sai na karbi tayin zama shugaba kawai, domin na kwato kasar nan daga afkawa cikin wani mummunan hali. Ni kuma na ce musu, na amince da Abdulsalami, kawai mu goya masa baya.

“Yayin da ake cikin wannan tirka-tirka ne, wasu kananan hafsoshi sun yi ta yi min zagon kasa ni da Janar Useni. Sun yi amanna cewa muddin na zama shugaban kasa, to sun shiga uku, amma ni dama ba ni da sha’awar zama shugaban kasa ko rike wani babban mukami na siyasa.

“Yayin da na ce wa manyan hafsoshin da ke so na zama shugaba cewa ni ba na son zama, sai su ka ce min, ai kuwa sai na yi da-na-sanin rashin karbar wannan tayi da na yi. Da farko ban yarda da abin da su ka fada min ba, saboda na ga dai ni da Janar Abdulsalami shakikan abokai ne, tun daga lokacin da mu ke a matsayi Laftanar. Kuma tare mu ke yin wasan kwallon gora a Barikin Sojoji na 2 Mechanised Division, da Shehu ‘Yar’Adua da Useni.

“To mu na shiga cikin dakin taro, sai Abdulsalami ya fara raba takardu, kamar an je ne da shirin yin zabe. Dama kuma kowa daga wanda ya shiga wurin da Bebul, sai wanda ya shiga da Alkur’ani, saboda babu wanda ya san wanda za a ce shi ne za a rantsar ya zama shugaba.

Sai da aka yi ta faman shawo kan manyan hafsoshin nan domin su amince da Abdulsalami ya zama shugaban kasa,. Dalili kenan aka je da Bebul da Alkur’ani a wurin rantsuwar.”

Ya ce, “Yayin da zabe ya zo kai na, sai na mike tsaye na ce ai duk mun yarda cewa Janar Abubuakar shi ne zai zama shugaba kuma babban kwamandan askarawan kasar nan. Na kuma ce a kara masa girma zuwa Janar mai tauraro hudu, kuma ya na zaune kusa da ni. To kun ji yadda mu ka yi nasarar nada Abdilsalami shugaban kasa, duk kuwa da cewa kotu ta taba samun shi da laifin yin cuwa-cuwar kudin albashi.”

Bamaiyi ya ce ya na farin ciki cewa har yanzu takardar bayanin wannan taro ta na nan wacce wani mai suna T. Fagbemi ya rika rubuta abubuwan da suka wakana. Kuma takardar na dauke da cewa Bamaiyi din ne ya ce a nada Abdulsalami, kuma a kara masa girma zuwa Janar mai tauraro hudu.

Ya kara fada a cikin littafin nasa cewa ya yi nadamar yadda Abdulsalami ya canja bayan ya hau mulki.
Ya kara da cewa “sabon shugaban wanda ya yi mulki tsakanin 8 Ga Yuni, 1998 zuwa 29 Ga Mayu, 1999, sai ya fara kokwanton biyayya ta a gare shi, kuma ya fara yi min kallon wata barazana a gare shi.”

Dalilin da ya sa Bamaiyi ya fadi haka, shi ne, Bamaiyi bai goyi bayan yadda wasu tsoffin sojoji irin su Janar Babangida suka zartas cewa a dawo da Olusegun Obasanjo ya shugabanci Nijeriya.

“Abdulsalami ya rika yi taron sirri tsakanin sa da Janar Babangida da Janar Aliyu Gusau. Na rika samun rahoton yadda su ke haduwa wuri daya. Amma ni ban damu ba, saboda na san cewa ba wani dadewa za mu yi a gwamnati ba.

“Ashe ni ban sani ba, Janar Abdulsalami tuni shi da Babangida da TY Danjuma da Janar Aliyu Gusau duk sun amince Obasanjo ne zai dawo ya yi mulkin farar hula bayan saukar Abdulsalami. Ni kuma sai na tsaya kememe na ce ban yarda ba. Kuma haka na shaida wa gaba dayan su gaba da gaba.

To wannan matsayi da na dauka bai yi wa wadannan Janar-Janar dadi ba, sai shi kuma Janar Abubakar ya fara yin kaffa-kaffa da ni. Sai ya fara sa wasu jami’an leken asiri na sojoji su na rubuta rahotannin karya da kazafi kaina wai ni mutum ne mai cike da burin zama shugaban kasa. Domin bayan mutuwar Abacha babu wanda ya isa ya hana ni.”

Daga karshe Obasanjo ya ci zaben 1999, inda ya yi mulki daga 1999 zuwa 2007.

Tags: AbachaAbdussalamAso RockBamaiyiHausaLabaraiMagashiNigeriaPREMIUM TIMESVictor Malu
Previous Post

‘Yan sandan Britaniya sun tuhumi Ahmed Musa kan zargin dukar matar sa da yayi

Next Post

KANJAMAU: Yaduwar ta ya karu a sansanonin ‘yan gudun Hijira dake jihar Barno

Next Post
Mun koyo dabarun warkar da cutar tabuwar hankali a kasar Burundi da Rwanda – Likita Wakama

KANJAMAU: Yaduwar ta ya karu a sansanonin ‘yan gudun Hijira dake jihar Barno

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Sakamakon Zaɓen Kaduna: APC ta ba PDP ratan kuri’u 12,000 a jimlar kuri’un da aka bayyana na kananan hukumomi 22 saura karamar hukumar Kudan
  • ƘAURAN BAUCHI: Rundunar Bala ta tarwatsa Dakarun APC a Bauchi
  • BANKA WA GIDAN WUTA: Darasi da jan hankali ga Hukumar Tace Finafinai ta Kano
  • KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano
  • ZAƁEN GWAMNAN KEBBI: Hukumar Zaɓe ta bayyana zaɓen Kebbi, ‘INKONKULUSIB’

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.