Ma’aikatar kiwon lafiya na babban birnin tarayya ta sanar da mutuwan wani mutum daya yau a dalilin kamuwa da cutar sankarau.
An sanar da rasuwar wasu guda hudu jiya a unguwan Durumi ta dalilin kamuwa da cutar.
Sakataren hukumar cibiyoyin lafiya na matakin farko Rilwanu Mohammed ya shawarci mutane da su daina yin cinkoso a wuri daya sannan a dinga bude taguna da kofofi domin samun isasshen iska.
Yace anyi wa yara sama da 17,000 rigakafin cutar dake garuruwan dake babban birnin tarayyan.