Ministan Jiragen Sama Hadi Sirika yace maida ayyukan tashi da saukan jiragen sama zuwa Kaduna daga Abuja zai lashe kudade sama da naira biliyan 1.
Ministan ya fadi hakanne a wajen amsa gaiyatar da majalisar dattawa tayi musu domin bada bayanai akan dalilan da yasa dole sai an koma filin jirgin saman Kaduna don za’a gyara na Abuja.
A bayanin da yayi wa’yan majalisan Ministan yace za’a kashe ma hukumar Jargen kasa naira miliyan 100.9, hukumar kula da kiyaye hadura na kasa naira Miliyan 237.2, hukumar ‘Yan sanda naira miliyan 358.5.