Ministan Matasa da Wasanni Solomon Dalung ya jaddada kauna da goyon bayan sa ga shugaba Muhammadu Buhari da yake tattaunawa da wasu abokanan sa a Teburin Mai shayi a garin Jere.
Kamar yadda ya fadi a hirar sa da mai shayin yace babu wani a kasar nan da ya isa ya sake cin zabe wai don yana kudin siyan mutane.
” Duk wanda yake ganin zai ci Zabe a Najeriya da kudin sa A gaya masa watsiyar rakumi yayi nesa da kasa.”
Buhari Amanar Talakawa ne sannan mutane su sani Buhari bai taba neman Zabe ba sai dai a nemeshi yayi takara.
” Duk wanda yake ganin zai iya cin zabe a Nageriya da kudinsa, a gaya masa cewa wutsiyar rakumi yayi nesa da kasa.”
Discussion about this post