Jami’ar ‘Ecotes Benin University’ ta karrama Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya da digirin Dakta.
Shehu Sani ya sami wannan karrama ne ranar Asabar 15 ga watan Juli.
Mutane musamman ‘yan mazabar sanatan a Kaduna sun isar da gaisuwarsu ga sanatan a shafunan sadarwa na yanar gizo.
Adamu Abdullahi wanda ya na daya daga cikin wadanda suka tofa albarkacin bakinsu akai ya jinjina wa Sanata Shehu Sani kan wannan karramawa da ya samu.
Discussion about this post